Connect with us

News

‎Dan Fashi Ya Mutu A Hannun Jami’an Yansanda Bayan Ya Yi Yunkurin Tserewa Daga Ofishinsu

Published

on

IMG 6814

Rundunar ’yan sandan jihar Neja ta ce wani mutum da ake zargin ɗan fashi da makami ne, mai Suna Aliyu Salihu, ya mutu bayan harbin da jami’anta suka yi masa, lokacin da yake yunkurin tserewa daga ofishinsu na Maitumbi da ke Minna.

‎Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne misalin ƙarfe 9:20 na safiyar Asabar, lokacin da Salihu ya nemi fita don yin bayan gida.

Advertisement

Gwamnatin Tarayya Ta Ceto Daliban Da Aka Sace a Kebbi

‎ A cewar majiyar, daga nan sai ya kai wa jami’in da ke bakin aiki da kuma ɗaya daga cikin masu gadin ofishin duka, sannan ya tsallake katangar ofishin yana ƙoƙarin tserewa.

‎Daya daga cikin masu gadin ya bi shi, ya kuma yi harbi da nufin dakatar da shi, abin da ya jawo masa munanan raunuka. An garzaya da shi zuwa Asibitin ’Yan Sanda da ke Minna, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Advertisement

‎An ajiye gawar a Asibitin Tarayya Minna domin ƙarin bincike.

‎Rundunar ’yan sandan ta ce za ta gudanar da binciken cikin gida kan yadda lamarin ya faru da ko an bi matakan aikin rundunar yadda ya kamata.

Advertisement

 

Zagazola Makama 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending