Connect with us

News

An Kama Mutum 4 Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne Tashar Mota A Kano

Published

on

Har yanzu dai rundunar 'yan sandan jihar ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
Spread the love

An kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne ɗauke da makamai da ake zaton bindigogi ne a tashar mota ta Ƙofar Ruwa da ke Jihar Kano.

Tashar motar, wadda ke kusa da kasuwar kayan gini ta Ƙofar Ruwa a Ƙaramar Hukumar Dala.

Jami’an Yan Sanda Sun Haramta Goyo A Babura Masu Kafa 2 A Kano

A cewar mazauna yankin, an kama mutanen ne lokacin da suke ƙoƙarin shiga mota domin tafiya zuwa wani waje a cikin Kano.

“Mutanen da ke tashar motar ne suka lura da makaman da suke ɗauke da su. Take suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, waɗanda suka kama su. Su huɗu ne gaba ɗaya,” in ji Musa Balarabe, wani mazaunin yankin.

Advertisement

Ya ce an kama su ne da misalin ƙarfe 1 na rana.

Da farko an kai su ofishin ’yan sanda na Ƙofar Ruwa, kafin daga bisani aka mayar da su ofishin Dala.

Wani mazaunin yankin, Umar Nuhu, ya ce yana cikin shagonsa da ke Kwanar Taya, kusa da ofishin ’yan sandan, lokacin da aka kawo mutanen.

Ya ce hakan ya jawo firgici, inda mutane suka fara gudu a ko’ina.

Advertisement

Nuhu, ya ƙara da cewa mutane da yawa sun yi dandazo a ofishin ’yan sandan, yayin da wasu matasan ke son ɗaukar doka a hannu.

Da aka tuntuɓi kakakin ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, bai ce komai kan lamarin ba.

Ya ce har yanzu suna tattara bayanai kafin su fitar da sanarwa.

 

Advertisement

 

AMINIYA

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *