Connect with us

News

Wasu Bata-gari Sun Hallaka Wata Mata Mai Juna Biyu Da Ɗanta A Kano  ‎

Published

on

Unguwa gawa

Mazauna unguwar Sheka Sabuwar Gandu da ke cikin birnin Kano sun shiga firgici, bayan wasu da ba a san ko su waye ba sun kashe wata mace mai juna biyu tare da ƙona ta ita da ɗanta mai watanni 18.

‎Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Asabar, lokacin da mijin matar ya dawo gida daga wurin aiki da misalin ƙarfe 8 na dare, inda ya tarar da ƙofar gidansa a kulle daga waje.

Advertisement

Gwamnatin Tarayya Ta Haramtawa Ɗaliban SS2 Zana Jarrabawar Kammala Sakandire 

‎An ce bayan ya balle ƙofar, sai ya shiga ya tarar da gawar matarsa da ɗansu a kwance, bayan an kai musu hari tare da ƙona su, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin alhini da firgici.

‎Wani jagoran al’umma a yankin, Ahmad Sani, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai nuna damuwa kan ƙarancin tsaro da yankin ke fuskanta.

Advertisement

‎A cewarsa, mazauna unguwar sun gina ofishin ‘yansanda domin ƙarfafa tsaro, amma har yanzu ba a tura jami’an tsaro domin kula da ofishin ba.

‎Ya yi kira ga Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kano, Ibrahim Bakori, da ya gaggauta ɗaukar mataki ta hanyar tura jami’an tsaro zuwa yankin domin hana sake aukuwar irin wannan hari.

Advertisement

‎Da aka tuntubi Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ‘Yansanda a Jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna, ya tabbatar da faruwar lamarin.

‎Ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike, tare da tabbatar da cewa za a kamo waɗanda suka aikata laifin domin gurfanar da su gaban kotu.

Advertisement

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending