Connect with us

News

Yan Jarida 7 Sun Rasa Rayukansu Sakamakon Mummunan Hatsarin Mota A Gombe 

Published

on

1767047068445
Spread the love

Ma’aikata shida na Gidan talabijin na Kasa (NTA) da ke Gombe sun rasu, wasu hudu sun jikkata a wani hatsarin mota a kan hanyar Gombe-Yola.

Hatsarin ya auku ne a Karamar Hukumar Kaltungo da ke Jihar Gombe a yayin da suke dawowa daga bikin auren abokin aikinsu

Gwamnatin Kano Ta mika sakon Ta’aziyyar Rasuwar Barrista Maryam Abubakar

An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti domin kulawar gaggawa, bayan tayar motarsu ta fashe a yankin Ladongor, tsakanin Billiri da Kumo a kan hanyar Gombe-Yola.

Hukumar Kiyaye Lafiyar Hanya (FRSC) ta Gombe ta bayyana cewa mutane 11 ne ke cikin motar Hummer da ta yi hatsarin.

Advertisement

Shugaban tawagar FRSC, AM Saddam, ya ce mutane biyar sun mutu, yayin da maza uku da mace ɗaya ke samun kulawa a Asibitin Kwararru na Gombe.

Ya ƙara da cewa, “An fara kai waɗanda abin ya shafa zuwa Amana Clinic da Babban Asibitin Billiri, daga bisani aka kwashe su gaba ɗaya – waɗanda suka mutu da kuma masu jikkata – zuwa Asibitin Kwararru na Gombe.”

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *