Connect with us

News

Ba zaben 2027 ne ya dami Gwamnan Kano Abba Yusuf ba a yanzu – Waiya ‎ ‎

Published

on

waiya 1365x2048 1
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bai mayar da hankali kan batun zaɓen 2027 ba a halin yanzu, sai dai kan kokarin samar da ci gaba da inganta rayuwar al’ummar jihar.

Waiya ya bayyana hakan ne yayin wani taro da tsofaffin Ƙansilolin kananan hukumomi suka gudanar domin yin mubaya’a ga Shugaban Riƙon Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano, Hon. Abdullahi Zubairu Abiya.

Tsofaffin Ƙansilolin Jihar Kano Sun Yi Mubaya’a ga Shugaban Riƙo na NNPP na Jihar Kano Hon. Abdullahi Zubairu Abiya

A cewarsa, sau da dama a yayin zaman majalisar zartarwa, idan aka ambaci batun zaɓe mai zuwa, Gwamna Abba Kabir Yusuf kan jaddada cewa ba lokacin siyasa ba ne, face lokacin aiwatar da manufofin da za su amfani jama’ar Kano.

“Abin da ke gaban gwamnan Kano a yanzu shi ne cigaban jihar da walwalar ‘yan Kanawa. Zaben 2027 ba shi ne abin da ke damunsa ba,” in ji Waiya.

Ya kara da cewa gwamnatin jihar ta mayar da hankali ne kan muhimman bangarori kamar ilimi, kiwon lafiya da bunkasa rayuwar matasa, domin tabbatar da ci gaba mai dorewa.

Wannan bayani na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan yiwuwar hadakar jam’iyyun adawa gabanin babban zaɓen 2027 a Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending