News
Da Dumi-Dumi :An ga watan Ramadan a Saudiyya
Hukumomin kasar Saudiyya sun umurci a fara azumi daga gobe Labaraba, 18 ga watan Fabareru na 2026
A yau Talata ne rahotanni ke cewa an ga jinjirin watan azumin Ramadan a sassa daban daban na kasar Saudiyya.
Jami’an ’Yan Sanda Sun Ceto Mutumin Da Zargi Mahaifinsa Ya Daure Shi Da Sarka Tsawon Shekaru 17
Hukumomi sun umurci a fara azumi daga gobe Laraba.
Shafin Haramain Sharifain ne ya ruwaito hakan, inda ya ce, “an ga jinjirin watan Ramadan na shekarar 1447 wato shekarar 2026 a Saudiyya.
Tunda farko babbar kotun Ƙolin Saudiyya ce ta yi kira ga dukkan Musulmi a faɗin ƙasar da su fita domin neman jinjirin watan Ramadan a yammacin ranar Talata, 29 Sha’aban 1447AH, daidai da 17 ga Fabrairu, 2026 bisa kalandar Umm Al-Qura.
Sanarwar ta kara da cewa za’a fara Sallar Asham a kasar musamman masallacin Ka’aba da na Madina wato Masallacin Annabi Muhammad SAW.
