Connect with us

News

Falalar Da Ke Tattare Da Azumin Watan Ramadan

Published

on

ramadan 2022 quotes and messages e1648827203929

Falalar da ke tattare da azumin watan Ramadan

 

Advertisement

Azumin watan Ramadan rukuni ne daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma farilla ne da Allah ya wajabta a kan bayinsa.

Azumi yana da falala mai girma, da lada mai yawa ribi-ribi. Allah Madaukakin Sarki ya raba azumi zuwa gare Shi, saboda girmama shi da daukaka shi.

Advertisement

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Azumi na da falala mai tarin yawa, amma ga wasu daga cikin su:

Advertisement
  1. A watan Ramadan ana bude kofofin Aljannah, sannan ana rufe kofofin wuta, kuma ana daure shaidanu, zuciya tana fuskantar aikin alheri.
  2. Yin azumi da tsayuwar sallar ashan saboda Allah da neman lada, yana gafarta abin da ya gabata na zunubai.
  3. A cikin watan Ramadan akwai daren Lailatul-Kadari, duk wanda ya tsaya a cikin wannan dare yana mai imani da Allah da neman lada to za a gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa.
  4. Umara a cikin Ramadan tana daidai da yin aikin hajji tare da Manzon Allah (SAW).
  5. Watan Ramadan watan Alkur’ani ne, a cikinsa aka saukar da shi, don haka ya dace a yawaita karanta shi a cikin wannan wata.
  6. Watan Ramadan wata ne na kyauta da ciyarwa da sadaka.
  7. Baccin mai azumi ibada ne.
  8. Mai azumi yana tare da farin ciki biyu;

a. Yayin da ya ke buda baki da,

b. Lokacin da zai hadu da Allah (S.W.A).

9. Azumi garkuwa ne ga wutar Jahannama.

Advertisement

 

10. Watan Ramadan wata ne da Allah ke ’yanta bayinsa daga wuta.

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending