Connect with us

News

Iran Ta Kai Hare-hare Da Makamai Masu linzami Kan Birane Da Dama Na Isra’ila

Published

on

FB IMG 1727802323931

Iran ta sake kai hare-hare sassan Isra’ila ta hanyar amfani da makamai masu linzami waɗanda a wannan karon ta yi ruwansu lokaci guda a yankunan kudanci da arewacin ƙasar.

Kafin yanzu Iran na kai hare-hare ne daban daban ko dai a yankin Arewacin Isra’ilar ko kuma kudanci saɓanin wanda aka gani a yau Litinin dai dai lokacin da ake shiga kwana na 9 da faro yaƙin ƙasashen.

Advertisement

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Garin Maƙarfi A Jihar Kaduna

An ji ƙarar kuwwar ankararwa a birane da dama na Isra’ilar tun daga Haifa har zuwa Dimona.

Advertisement

Duk da cewa Isra’ila ta yi nasarar tare wasu daga cikin makaman masu linzami amma bayanai sun ce hare-haren na Iran sun yi gagarumar ɓarna.

Bayanai sun ce hare-haren sun shafi yankunan Tel Arad da Dimona waɗanda ke gaba da Negev, wato yankin da cibiyar binciken makaman nukiliya na ƙasar ya ke.

Advertisement

Haka zalika an ji kuwwar ankararwa a Tiberias da tsaunukan Jezreel kana Beisan da kuma kwarin Galilee.

Bayanan da Isra’ila ta fitar ta ce ta sanya kuwwar ne don ankarar da jama’arta amma ba don hare-haren na Iran sun yi mata illa ba.

Advertisement

Mazauna yankunan da Iran ta harba makaman dai sun ce sun ji ƙarar fashe-fashe sai dai babu tabbacin ko ƙarar daga tare makamin ne ko kuma daga saukar shi.

 

Advertisement

RFI

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending