News
Ministan Tsaron Ya Gayyaci Shugabannin Rundunonin Soji Kan Karuwar Hare-hare A Arewa
Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya gayyaci dukkan shugabannin rundunonin sojin Najeriya zuwa ofishinsa domin gudanar da wani muhimmin taro kan sababbin hare-haren da aka kai kan sansanonin soji daban-daban a yankin Arewa maso Gabas.
Waɗanda zasu halartar taron a hedikwatar Ma’aikatar Tsaro da ke Abuja sun haɗa da Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede, da Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu.
Ƴan Daba Sun Kashe Matashi Dan Kwamitin Tsaro A Kano
Sauran sun haɗa da Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, da Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Idi Abass, tare da wakilai daga Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa da sauransu.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a baya-bayan nan, ‘yan ta’adda sun kashe akalla kwamandoji uku na soji masu mukamin Laftanar-Kolonel a jihar Borno.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
