Connect with us

News

An Sanya Dokar Hana Fita Ta Sa’o’i 48 A Jos ‎

Published

on

filato

Gwamnatin Jihar Filato ta sanar da ƙaddamar da dokar hana fita ta sa’o’i 48 a Jos ta Arewa. Matakin ya biyo bayan wani hari da ya auku a Gari Ya Waje ranar Lahadi, 29 ga Maris, 2026.

A cewar sanarwar, dokar za ta fara aiki daga ƙarfe 12 na dare na 29 ga Maris. Za ta ƙare ranar 1 ga Afrilu, 2026, domin bai wa jami’an tsaro damar daidaita al’amura.

Advertisement

Sheikh Pantami Ya Roƙi El-Rufai, Ribadu Da Uba Sani Su Sulhunta A Jana’izar Mahaifiyarsa

‎Gwamnatin jihar, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Caleb Mutfwang, ta yi Allah-wadai da harin. Ta ce za a kamo masu hannu cikinsa tare da gurfanar da su gaban shari’a.

Advertisement

‎Hukumomi sun buƙaci jama’a su kwantar da hankula su kuma bi umarnin tsaro. An roƙe su su ba da bayanai masu amfani don taimaka wa bincike.

‎Sanarwar da Kwamishinar Yaɗa Labarai, Joyce Ramnap, ta sanya wa hannu ta jaddada ƙudirin gwamnati na kare rayuka da dukiyoyi.

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending