News
Rajistar Zaɓe a Kano: Sama da Mutane 10,000 Sun Yi Rijista Cikin Kwanaki Shida
A Jihar Kano, sama da mutane 10,000 ne suka yi rajistar katin zaɓe na dindindin (PVC) cikin wani babban shirin rajista na kwanaki shida da aka gudanar a dakin wasanni na Kofar Mata.
Shugaban kwamitin sa ido kan rajistar masu zaɓe kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin kammala shirin.
Ya ce, duk da cewa yawan mahalarta ya nuna alamar ƙarfafawa, har yanzu akwai buƙatar ƙara wayar da kan jama’a domin jawo hankalin ƙarin mutane su yi rajista.
A cewarsa, an samu matsakaicin mutane 1,500 da ke yin rajista a kowace rana a cikin kwanaki biyar na farko, yayin da a rana ta ƙarshe aka samu fiye da mutane 2,000.
Waiya ya yaba da ƙoƙarin Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), musamman Kwamishinan zaɓe na jihar, Ambasada Abdu S. Zango, bisa yadda suka gudanar da aikin cikin tsari da ƙwarewa.
Sai dai ya jaddada cewa, wannan nasara ya kamata ta zama kira ga waɗanda har yanzu ba su yi rajista ba, yana mai cewa katin zaɓe shi ne muhimmiyar hanyar da ‘yan ƙasa ke amfani da ita wajen tasiri a harkokin mulki.
Haka kuma ya tunatar da jama’a cewa rajistar zaɓe za ta ci gaba har zuwa watan Agustan 2026 a dukkan ofisoshin INEC da ke ƙananan hukumomi 44 na jihar.
Ya kuma yaba da rawar da ɗalibai masu aikin sa kai daga manyan makarantu tara suka taka, musamman wajen taimaka wa rajistar farko ta yanar gizo.
A nasa ɓangaren, shugaban sashen fasahar sadarwa na INEC, Edwin Ocheka, ya ce hukumar na da shirin ci gaba da inganta aikin rajistar tare da tabbatar da gaskiya da inganci.
Masu ruwa da tsaki sun ce mataki na gaba shi ne ƙara wayar da kai da kuma sauƙaƙa hanyoyin rajista domin tabbatar da cewa kowa da kowa da ya cancanta ya samu damar shiga cikin harkokin dimokuraɗiyya.
