News
Gwamnatin tarrayya Ta Janye Tuhumar Da Ta Ke Yiwa Malami Kan Ta’addanci
Mai gabatar da ƙara Akinlolu Kehinde ya sanar da matakin yayin zaman kotu na yau, inda ya ce za su ci gaba da tuhumar Malami a kan wasu batutuwa daban da suka shafi halarta kuɗaɗen haramun.
Lauyan Malami, Shaibu Aruwa ya shaidawa mai shari;a Joyce Abdulmalik cewar sun samu takardar yiwa tuhumar garambawul.
A watan Disambar 2025 ne gwamnatin ta zargi Malami da ɗan sa, da shirin aikata laifukan ta’addanci, saboda mallakar wasu muggan makami ba tare da izini ba.
Dama dai tun lokacin da aka gurfanar da Malami da ɗansa Abdul’aziz a gaban kotu, sun ƙi amincewa da zargin da ake musu na aikata laifukan ta’addancin, da a yanzu aka wanke su.
Advertisements
