News
Dakarun Soji Sun Hallaka Ƴan Ta’adda 1,500 A Cikin Watanni Shida
Dakarun soji a sassan Najeriya sun kashe ƴan ta’adda dubu 1,597 tare da ceto mutane dubu 1,516 da aka yi garkuwa dasu cikin watanni shida na farkon shekarar 2026.
An sanar da wannan nasara ne yayin wani taron tsaro da aka gudanar a cibiyar yaƙi da ta’addanci a Abuja, inda mai magana da yawun rundunar sojin da wakilan sauran hukumomin tsaro 14 suka gabatar da rahotan ayyukansu.
An Kama Wani Mutum Bisa Zargin Sayar Da Ɗan Abokinsa Kan Naira Miliyan 1.3
A cewar mai magan da yawun rundunar Samaila Uba, sojojin sun kai hare-hare ta ƙasa da sama da kuma ta ruwa har sau dubu 14,221, tsakanin Janairu zuwa Yunin bana a faɗin yankunan ƙasar 6.
Hare-haren sun shafi kan ƴan ta’adda, da ƴan bindiga, da masu garkuwa da mutane, da masu satar mai ta hanyar fashe-fashen bututu, da dai sauran laifuffuka.
Yayin hare-haren, jami’an tsaron sun ƙwato bindigu 451, da alburusai dubu 16,726 dai dai sauran makamai da ƴan ta’addan ke amfani dasu..
-
News6 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
-
Uncategorized2 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
