Connect with us

News

“Ku Yi Aiki Ko Ku Sauka” — Gwamnan Kano Ya Gargaɗi Masu Riƙe Da Muƙaman Gwamnati

Published

on

1783243186531

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci sakaci ko gazawar masu riƙe da muƙaman gwamnati ba, inda ya bayyana cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin da aka ɗora masa ba ya kamata ya ajiye muƙaminsa.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), inda ya jaddada cewa sakamakon aiki ne kaɗai ma’aunin tantance nasarar jami’an gwamnati.

Saraki Ya Ɗauki Nauyin Ragowar Kuɗin Karatun Ɗalibar UNILORIN Mai First Class Zuwa Italiya

Kalaman gwamnan sun sake haifar da muhawara kan muhimmancin shugabanci nagari, gaskiya da kuma ɗaukar alhakin gudanar da ayyukan gwamnati domin tabbatar da cewa al’umma na cin moriyar manufofin da gwamnati ke aiwatarwa.

Binciken da gudanar kan yadda ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnatin jihar ke aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati, tare da tambayar ko ayyukansu na cika tsammanin al’ummar Kano.

Rahoton ya kuma nuna cewa ƙarfafa ingantaccen shugabanci, bayyana ayyukan gwamnati ga jama’a da inganta gaskiya wajen gudanar da mulki na daga cikin hanyoyin da za su ƙara amincewar al’umma ga cibiyoyin gwamnati tare da tabbatar da ingancin ayyukan gwamnati.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending