Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Yin Bincike Kan Ma’aikatar Bogi Da Ake Ta Takaddama A Kai

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bai wa hukumar ICPC umarnin gudanar da bincike kan badaƙalar ma’aikatar bogin nan ta PFIPC da ake ta taƙaddama akai.

Wannan dai ya biyo bayan caccaka da gwamnatin ke ci gaba da sha daga ƴan adawa da ƙungiyoyin fararen hula da kuma ƴan Najeriya, kan yadda ake zargin wata ma’aikata na wanzuwa ba tare da sanin gwamnati ba.

An samar da shafin Facebook mai suna “Tsaro da Shari’a” domin kawo sahihan labaran Tsaro da Shari’a.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Bayo Onanuga ya fitar yau Talata, Tinubu umarci gudanar da binciken tare da miƙa masa rahotansa cikin kwanaki 30.

Wani mutum Adeniyi Adeyimi Mattew ne ya ayyana kansa a matsayin babban daraktan wannan ma’aikata ta PFIPC da ke haɓaka hulda da zuba jari daga ƙasashen waje.

Cikin zarge-zargen da ICPC za ta bincika sun haɗa da yadda Adeyemi ya samu takardar naɗa shi shugabancin ma’aikatar da kuma sauran takardu na hukumomin gwamnati.

Advertisement

Akwai kuma batun yin amfani da muƙamin wajen samun karbuwa a hukumace tare da samun tallafin jami’an diflomasiyya, ciki har da batun takardun biza da buɗe asusun bankin ta hanyar amfani da takardun gwamnati na ƙarya.

Tinubu ya umarci dukkan ma’aikatu da hukumomi da rassa na gwamnatin tarayya da su bai wa ICPC bayanan da suke dasu, wanda zai taimaka mata a binciken.

Shugaban Najeriya ya kuma ce duk wanda aka samu da hannu a wannan badaƙala to zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

 

 

 

Advertisement

RFI

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending