News
Rikici Ya Barke A Majalisar Wakilai Kan Buƙatar Gayyatar Shugaba Tinubu
An samu zaman cike da cece-kuce a Majalisar Wakilan Tarayya a yau ranar Laraba bayan wasu ‘yan majalisar sun yi sabani kan wani ƙuduri da ke neman a gayyaci Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, domin ya yi bayani kan wasu batutuwa da suka shafi kuɗaɗen gwamnati.
Hatsaniyar ta fara ne a yayin zaman majalisar lokacin da ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Okpe/Sapele/Uvwie ta jihar Delta, Benedict Etanabene, ya tashi da batun gaggawa (Point of Privilege).
Jami’an Ƴansanda Sun Kama Wani Sufeton Bogi
Etanabene ya jawo hankalin majalisar zuwa wata takarda da Akanta Janar na Tarayya, Shamseldeen Ogunjimi, ya fitar a ranar 29 ga Yuni, wadda ta shafi wasu muhimman batutuwan gudanar da kuɗaɗen gwamnati.
Sai dai yayin da aka fara tattaunawa kan buƙatar gayyatar Shugaba Tinubu, wasu ‘yan majalisar sun nuna adawa da hakan, yayin da wasu kuma suka goyi bayan a ci gaba da tattaunawa.
Wannan ya janyo hayaniya da cacar baki a zauren majalisar, lamarin da ya sa aka ɗan dakatar da zaman na wani lokaci kafin a ci gaba.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a cimma matsaya ta ƙarshe kan ko za a gayyaci Shugaba Tinubu ko a’a ba.
-
News7 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized3 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
