Connect with us

News

INEC Ta Sanya Ranar Zaɓen Cike Gurbi A Jihohin Kano, Gombe, Bauchi Da Delta

Published

on

‎Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanya ranar Asabar, 19 ga Satumba, 2026, domin gudanar da zaɓen cike gurbi a jihohin Kano, Gombe, Bauchi da Delta.

‎Sakataren Yaɗa Labaran Hukumar, Tunde Oketola, ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ranar Talata a Abuja.

Jami’an Ƴansanda  Sun Ceto Yara 17 Da Aka Sace A Oyo

‎A Jihar Kano, za a gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Dokokin Jihar da ke wakiltar Dawakin Kudu.

‎A Gombe kuwa, za a gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai ta tarayya mai wakiltar Gombe/Kwami/Funakaye.

‎Hukumar ta ce zaɓen zai kuma gudana a wasu kujeru da suka zama babu kowa a jihohin Bauchi da Delta.

Advertisement

‎INEC ta bayyana cewa shirya zaɓen na daga cikin matakan da take ɗauka domin cike guraben kujerun siyasa da suka zama babu kowa kafin babban zaɓen 2027.

‎Hukumar ta ƙara da cewa za ta sanar da ƙarin bayanai kan tsarin gudanar da zaɓen da sauran shirye-shiryen da suka shafi zaɓen a lokacin da ya dace.

 

 

Vanguard

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending