Connect with us

News

Dan Siyasa Ya Yi Karar Bokansa A EFCC Bayan Faduwa Zaben Neman Takara

Published

on

 

 

Advertisement

DAGA KAHDIJA ABDULLAHI MAHMUD 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wani dan dan siyasa ya yi karar bokansa da malamin tsubbunsa a wajen Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arziki Zagon Kasa (EFCC) kan zargin damfararsa bayan ya fadi zaben neman takara

 

Advertisement

Jami’an EFCC sun damke boka tare da tsubbu ne bisa zargin damfarar dan dan siyasar da ba a bayyana sunansa ba Naira miliyan 24.

Ba za a shawo kan matsalar sufurin jiragen sama nan kusa ba a Najeriya – Minista

Advertisement

 

Jaridar PM ta ruwaito cewa wadanda ake zargin sun bugi hancin dan siyasar ne cewa za su yi msihi aiki ya ci zaben takarar Dan Majalisar Dokokin Jihar Ekiti, amma ya sha kaye.

Advertisement

 

Mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren ya ce a ranar 7 ga Yulin 2022 aka damke su a Ado-Ekiti, Jihar Ekiti, bayan an kai karar su gaban hukumar a kan abin da suka aikata.

Advertisement

 

Jami’in ya ce a lokacin da ake binciken su, bokan ya yi ikirarin ya karbi kudade daga hannun dan siyasar har ma da karin Naira 2.9 a matsayin kudin sayen shanu da raguna da sauran kayan aiki.

Advertisement

 

Da yake maida bayani, dan tsubbun ya ce, “Namu bai wuce yin addu’o’i da yanka abin yanka ba, sannan mu bar wa Allah sauran.”

Advertisement

 

Uwujaren ya ce za a gurfanar da su biyun a kotu nan ba da dadewa ba.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending