News
Tabarbarewar Tsaro Na Kara Firgita Jama’a A Sassan Najeriya
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Tabarbarewar tsaro a sassan Najeriya na kara firgita jama’a don yanda ba wanda ya tsira tsakanin fararen hula a kan titi da su kan su jami’an tsaron.
Labarin daukar karin matakan tsaro a cikin Abuja da Kano na daga lamuran da ke kara nuna ba a samu bakin zaren warware kalubalen tsaron.
Duk da ya ke dama a duk shekarar zabe ko yakin neman zabe a kan iya samun irin wannan barazana da kan hana mutane sukuni.
Rashin tsaron ya sa mutane na zama cikin takatsantsan da kuma yin addu’ar neman kariya daga Allah.
Shugaban amintattu na gamaiyar kungiyoyin arewa Nastura Ashir Sharif ya ce gwamnatin na baiyana cewa ta na ware makudan kudi kan tsaro amma kamar ba a gani a kasa.
Fadar Aso Rock dai kan ce a rika fidda siyasa a lamuran tsaro don har indai za a cimma nasara kan samar da tsaro sai kowa ya ba da hadin kai.
Lokaci-lokaci za ka ga an raba lambobin gaggawa na tuntubar jami’an tsaro don bugawa da zarar an ga abin da ba a amince da shi ba.
Shin lambobin su na amfani ko kuwa a’a, ingantar tsaron zai zama amsa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
