News
Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 10 a hare-hare kan Zirin Gaza
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Mutum aƙalla 10 Isra’ila ta kashe a hare-hare ta sama da ta kai kan Zirin Gaza, cikinsu har da kwamandan gwagwarmaya na Falasɗinawa a ranar Juma’a.
Hukumomin lafiya a yankin sun ce cikin waɗanda aka kashe akwai ƙaramar yarinya da kuma raunata wasu gommai.
Gwamnatin Najeriya ta nemi iyayen ɗalibai su roƙi ASUU ta janye yajin aiki
Firaministan Isra’ila ya ce an kai harin ne bayan samun “barazanar gaggawa” daga ƙungiyar Palestinian Islamic Jihad (PIJ) sakamakon kama ɗaya daga cikin mambobinta a farkon makon nan.
PIJ ta harba makaman roka fiye da 100 “a martanin farko da ta mayar”, in ji shi.
Rundunar sojan Isra’ila ta ce hakan ne ya sa ta fara luguden wuta a yammacin Juma’a ta hanyar kai wa sansanin ‘yan gwagwarmayar hari.
