News
Najeriya Ta Tabarbare Fiye Da Yadda Take A 2015 – Sunusi
Daga Yasir sani Abdullahi
Mai Martaba Sarkin Kano na 14 kuma Khalifan Tijjaniyya a Najeriya Muhammadu Sunusi na biyu, ya bayyana damuwa kan halin da Najeriya ke ciki, yana mai cewa, kasar nan ta tabarbare fiye da yadda take a shekarar 2015, lokacin da shugaba Muhammadu Buhari ya karbi mulki daga hannun Goodluck Jonathan.
Khalifa Sunusi na magana ne a wurin wani taro da Gidauniyar Akinjide Adeosun ta shirya kan sha’anin shugabanci a birnin Lagos.
A cewar sa “Wannan ita kadai ce kasar da ke samar da man fetur amma take kokawa a halin yanzu bayan da farashin man ya tashi sakamakon rikicin Rasha da Ukraine.
Yace “Daukacin kudaden shigarmu ba za su iya biyan basukanmu ba.”
Khalifa Sunusi ya kuma yi gargadin cewa, abin da aka gani a 2015 nafila ne kan abin da zai faru a 2023, yana mai cewa, a halin yanzu Najeriya na fama da matsaloli da dama da suka hada da ta’addanci, hare-haren ‘yan bindiga da tsadar rayuwa da rashin tabbas kan farashin kudaden ketare.
Khalifan ya kuma ɗiga ayar tambaya yana mai cewa, ta yaya ne tarihi zai tuna shugaban kasa da gwamnoni da ministoci da suka shafe tsawon shekaru 8 kan karagar mulki?
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
