News
Ɗan makaranta ya harbe ɗan ajinsu kafin ya kashe kansa
Daga Usman Abdullahi jibiri Ngurun Yobe
Wani ɗan makaranta mai shekara 16 a Afirka ta Kudu ya harbe ɗan ajinsu biyo bayan wata rigima tsakaninsu, inda daga baya ya kashe kan sa.
Yaran suna mataki na 10 a Sakandaren Lesiba da ke Daveyton.
Hukumomi sun ce an yi harbin ne ranar Laraba yayin da aka koma sabon zangon karatu.
‘Yan sanda na gudanar da bincike kan lamarin kuma an tura jami’an kula da lalurar ƙwaƙwalwa da zimmar duba lafiyar waɗanda abin ya ritsa da su.
Advertisements
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
