Connect with us

News

Kotu a Kenya ta fara zaman sauraron karar sakamakon zaben shugaban kasar

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

Kotu a Kenya ta fara zaman sauraron karar zaben shugaban kasa da ke kalubalantar sakamakon zaben 9 ga watan Agusta.

Advertisement

 

Lauyoyin da ke wakiltar daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasar, Raila Odinga na gabatar da kararsu na neman soke nasarar da William Ruto ya samu a matsayin zabbabben shugaban kasar.

Direban adaidaitasahu ya mutu a kogi a Kano

Lauyoyin Mista Ruto da kuma wadanda ke wakiltar hukumar zaben za su bayyana a gaban kwamitin alkalai bakwai .

 

A halin yanzu, ana bincike da sake kirga kuri’u a rumfunan zabe 15 da aka kalubalanci sahihancinsu a kotu.

Advertisement

 

Al’ummar Kenya na bibiyar sauraron karar da ake watsa wa a gidajen talabijin din kasar.

 

Ana sa ran yanke hukunci a ranar 5 ga watan Satumba.

 

 

Advertisement

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending