News
Kotu a Kenya ta fara zaman sauraron karar sakamakon zaben shugaban kasar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotu a Kenya ta fara zaman sauraron karar zaben shugaban kasa da ke kalubalantar sakamakon zaben 9 ga watan Agusta.
Lauyoyin da ke wakiltar daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasar, Raila Odinga na gabatar da kararsu na neman soke nasarar da William Ruto ya samu a matsayin zabbabben shugaban kasar.
Direban adaidaitasahu ya mutu a kogi a Kano
Lauyoyin Mista Ruto da kuma wadanda ke wakiltar hukumar zaben za su bayyana a gaban kwamitin alkalai bakwai .
A halin yanzu, ana bincike da sake kirga kuri’u a rumfunan zabe 15 da aka kalubalanci sahihancinsu a kotu.
Al’ummar Kenya na bibiyar sauraron karar da ake watsa wa a gidajen talabijin din kasar.
Ana sa ran yanke hukunci a ranar 5 ga watan Satumba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
