News
Kotu ta yi watsi da bukatar biyan Sunday Igboho N20b
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotun daukaka kara ta yi watsi da bukatar biyan Sunday Igboho naira biliyan 20 saboda asarar da ya yi a gidansa.
Da yake yanke hukunci a karar da babban attoni janar na kasa da hukumar kula da tsaron farin kaya da daraktan hukumar a jihar Oyo suka shigar a kan hukuncin mai shari’a Muslim Hassan na babbar Kotun Jihar Oyo ya yanke na cewa hukuncin da mai shari’a Ladiran Akintola, ya yanke na cewa a biya Igboho kudin ya sabawa ka’ida.
Ba za mu bari wani ya yi katsalanda was q a zabukan 2023 ba – Buhari
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa a ran 17 ga watan Satumban 2021, mai shari’a Akintola ya bukaci a biya Igboho naira biliyan 20 a matsayin kudin asarar kayaki da ya yi a gidansa bayan hari da ya yi zargi ‘yan bindiga suka kai masa ranar 1 ga watan Yuli wadda kuma ya sabawa umurnin babban attoni janar na kasa, Abubakar Malami da kuma hukumar tsaron farin kaya da suka kalubalanci hukuncin.
Mai shari’a Hassan ya ce babu wasu hujjoji da suka marawa hukuncin babbar kotun jihar ta Oyo.
Ya ce mai shari’a Akintola bai gano asarar da Igbohon ya ce ya yi ba a tsawon bincikensa, inda ya kara da cewa babu kwararan hujjoji da suka nuna yawan asarar da Igbohon ya yi a gidansa.
Mai shari’a Hassan ya kuma kara da cewa ba wata hujja ko bincike da ta nuna mutum biyu sun mutu yayin hari a gidan dan gwagwarmayar kamar yadda ya yi ikirari.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
