News
Shugabancin Nigeria ba,na malalaci bane cewar atiku Abubakar
Daga Yasir sani Abdullahi
Tsohon mataimakin shugaban kasar Nigeria Kuma Dan takarar shugabancin kasa a jam,iyyar PDP atiku abubakar ya,ce shugabancin Nigeria Sam Sam bana malalaci bane Wanda baisan yadda kasar ke tafiya,ba
Atikun ya bayyana hakane lokacin da yake tattaunawa da gamayyar kafafen yada labarai a jahar kano lokacin da ya kawo ziyarar kwanaki uku
Atiku Abubakar yace “Najeriya a yanzu bata da isassun ƴan sanda da zasu kare ƴan ƙasa, Najeriya na da al’umma da suka zarce miliyan ɗari biyu, amma ƴan sanda basu fi mutum dubu ɗari huɗu ba, a don haka bazasu iya tsare mutanen najeriya ba”.
“Shugabancin ƙasa kamar Najeriya ba na malalaci bane, lokacin ina mataimakin shugaban ƙasa, kowanne dare sai an kawo min rahoton bayanan tsaro na sirri, kuma sai na karance su, sannan na nemi Babban jami’in tsaro na ƴan sanda na tambayeshi me yasa abu kaza ya faru, sai a dauki matakin gaggawa,”. Inji Atiku Abubakar
Ya kara da cewa nigeria tana San shugaban kasar da zai jajirce wajan nuna jajircewar sa ga Al,umma Dan Basu tsaron da ya kamata domin magance matsalolin da ke addabar Yan kasar
Kuma ya zargi shugaban kasa muhammadu buhari da,gin daukar shawarar sa a lokacin shiyasa ya yabar jam,iyyar APC Kuma gashi kasar na bakutar irinsa da zasu kawo matsalolin tsaro
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
