News
Hukumar kashe gobara ta Kano ta ceci rayuka 91, dukiya ta N24. 9m a watan Agusta
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce ta ceci rayuka da dukiyoyi 91 da kudinsu ya kai Naira miliyan 24.9 daga aukuwar gobara 29 a watan Agusta.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Saminu Abdullahi ya fitar ranar Juma’a a Kano.
An tsare mawaƙi Ice Prince bisa zargin guduwa da ɗan sanda
Mista Abdullahi, ya ce mutane 11 ne suka rasa rayukansu yayin da gobara ta lalata dukiya ta Naira miliyan 8.3 a tsawon lokacin da ake bitar.
Ya ce ma’aikatar ta amsa kiraye-kirayen ceto 55 da kuma kararrawar karya 14 daga mazauna jihar.
Kakakin ya bukaci jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen gudanar da ayyukan da suka shafi gobara domin hana afkuwar hadura.
Ya kuma gargadi masu ababen hawa da su rika tukin mota tare da kula sosai domin gujewa hadurra musamman a lokacin damina.
DAILY NIGERIAN
