Hukumar Hisbah ta jihar Kano da ke arewacin Najeirya ta ce ta fara kama mabaratan da ke yawo a kan titunan jihar.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ambato babban kwamandan hukumar Muhammad Harun Ibn Sina, wanda ya bayyana haka ga manema labarai a birnin Kano na cewa kawo yanzu hukumar ta kama mabarata kusan 930 cikin makonni biyu.
Nijeriya komai ya lalace a mulkin APC – Makarfi
Hukumar dai na zargin mabaratan da zama masu leken asiri ga ‘yan ta’adda, abin da kuma ke yi wa tsaron jihar barazana.
Ibn Sina ya kara da cewa da yawa da cikin mabaratan wadanda matasa ne da matan aure wadanda ke gararamba a kan titunan jihar na fakewa da bara wajen aikata laifukan da suka hadar da karuwanci, da kwacen wayoyin hannu.
