Connect with us

News

Ambaliya na barazana ga sama da mutum miliyan 100 a Pakistan

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

 

 

 

Hukumomi a Kudancin Pakistan sun umarci mutane kusan 100,000 da su bar gidajensu a kokari da ake na kare su daga ɓallewar wata madatsar ruwa a wani babban tafkin kasar.

Advertisement

 

Mutane a lardin Sindh na cikin barazana sakamakon shiga gidajensu da ruwa daga kogin Manchar ke yi , inda jami’ai suka ce sun fara ɗaukar matakai domin kare ɗumbin al’ummomi a yankin.

Gasar Premier: Manchester United ta doke Arsenal 3-1

Ba a dai san hakikanin mutanen da za su bar gidajensu ba, inda ake samun kwararar jama’a zuwa tantunan wucin gadi da aka samar.

 

Pakistan dai na cikin mawuyacin hali bayan mummunar ambaliya ta makonni da ta shafi al’ummomi sama da miliyan 30.

Advertisement

 

Hukumomi na kuma cikin shirin ko-ta-kwana saboda hasashen samun mamakon ruwan sama a arewacin kasar cikin kwanaki masu zuwa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending