Connect with us

News

Hukumar Kwastam ta kama mazakutar jaki 7,000 da ake shirin fita da su waje

Published

on

Jaki

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar kwastam a Najeriya ta ce ta yi nasarar hana fita da mazakutar jakuna 7000 da aka yi shirin safarar su zuwa Hong Kong.

Advertisement

 

Kwastam ta yi wawan kamun ne ranar Laraba a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke birnin Lagos.

Advertisement

Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan bindiga a hanyar Kaduna zuwa Zaria

Kwantirola mai kula da filin jirgin sama Sambo Dan Galadima ne ya tabbatar da hakan a tattaunawarsa da BBC ranar Laraba, yana mai cewa an nade mazakutar jakunan ne a cikin buhunhuna 16.

Advertisement

 

Dan Galadima ya kara da cewa wadanda ake zargi da yunkurin safarar kayan sun tsere daga filin jirgin, a lokacin da jami’an kwastam suka nuna shakkun kan abin da ke cikin buhunhunan, sakamakon warin da ya turnuke wurin lokacin binciken kayan.

Advertisement

 

Darajar kayan dai ta kai sama da naira, 216,212,813.58.

Advertisement

 

Najeriya ta haramta safarar fatu ko duk wani abu da ya shafi jaki zuwa kasashen ketare, sakamakon karancinsu da ake fuskanta a kasa.

Advertisement

 

Kasashen yankin Asiya kamar China, yankin Hong Kong, da Koriya ta Kudu, da sauransu, na amfani da shi wajen yin magungunan gargajiya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending