Connect with us

Business

Najeriya za ta ci tarar kamfanonin jiragen sama kan kin saida tikiti da Naira

Published

on

Tuni jiragen kasashen waje irinsu Emirate suka dakatar da sufuri a Najeriya duk kan batun syan tikiti da naira maimakon dalar Amirka

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

 

Advertisement

Gwamnatin Najeriya ta yi barazanar sanya tara ga kamfanonin jiragen sama na kasashen waje, da suka ki amincewa da sayan tikiti da naira maimakon dalar Amirka.

 

Ministan sufuri, Hadi Sirika, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a wani bangare na taron majalisar zartaswa da shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar gwamnati da ke Abuja.

Napoli ta lallasa Liverpool da ci 4-1 a gasar cin kofin zakarun Turai

Sirika ya kara da cewa, bayanan sirrin da suka samu na cewa wasu daga cikin kamfanonin jiragen saman, sun ki amincewa su karbi Naira, kuma hakan ya sabawa dokokin Najeriya.

 

Advertisement

Ya kara da cewa, am bai wa ma’aikatar sufurin jirgin sama ta Najeriya umarnin magance matsala irin wannan da daukar mataki kan kamfanonin da suka nemi take doka.

 

A karshe Sirika ya yi kira u daina amfani da kafafen sda zumunta wajen bayyana bukatun da suke bukata daga gwamnatin Najeriya, maimakon haka su tun kari gwamnati gaba gadi domin bin matakan diflomasiyya wajen magance duk wata matsala.

 

Rashin dalar Amirka da Najeriya ke fama da karancin ta ya janyo kamfanonin jiragen kasashen waje kamar Emirate mallakin hadaddiyar daular larabawa, dakatar da zuwa kasar.

 

Advertisement

 

 

BBC NEWS

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending