Connect with us

News

Hajj 2022: Gwamnatin Zamfara ta mayar wa alhazai 1,318 naira 50,000 kowanne

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnatin jihar Zamfara ta mayar wa da kowane mahajjaci daga cikin alhazai 1, 318 da suka yi aikin hajjin bana zuwa kasar Saudiyya Naira dubu 50.

 

Advertisement

Gwamna Bello Matawallle wanda ya bada umarnin mayar da kuɗaɗen, ya umurci hukumar alhazai ta jihar da ta tabbatar da aiwatar da wannan umarni cikin gaggawa.

Saudiya ta baiwa alhazan Ummara damar zama a ƙasar har tsawon watanni 3

Advertisement

Ya umurci hukumar da ta fara biyan kuɗin daga nan zuwa ranar Litinin, 12 ga Satumba, 2022 a kowace karamar hukuma 14 na jihar.

 

Advertisement

Don haka, an shawarci maniyyatan da abin ya shafa da su je karamar hukumar inda suka biya kudinsu domin karɓar Naira 50,000 daga ranar Litinin 12 ga Satumba, 2022.

 

Advertisement

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin sakataren gwamnatin jihar (SSG), Alhaji Kabiru Balarabe ta ce matakin na ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin jihar ke ɗauka na rage wahalhalun tattalin arziki da ake fuskanta a kasar.

 

Advertisement

Balarabe ya ce gwamnati za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace don tallafa wa jama’a don inganta tattalin arzikinsu, jin dadinsu da kuma daukaka darajar rayuwarsu da walwala.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

DAILY NIGERIAN

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending