News
Yanzu-Yanzu: Jami’an DSS Sun Afka Gidan Mamu Dake Kaduna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) sun kai farmaki gidan wani mai tattaunawa da yan ta’addan da aka kama, Tukur Mamu a Kaduna da sanyin safiyar yau Alhamis. Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
‘Yan sandan sun zo ne a cikin motoci kusan 20 a wani abin da wani shaida ya bayyana.
Hajj 2022: Gwamnaptin Zamfara ta mayar wa alhazai 1,318 naira 50,000 kowanne
“Sun far wa gidan tare da kwashe takardu, wayoyi da kwamfutoci. An umurci wadanda ke cikin gidan da su sanya hannu a kan takardar da ba su karanta ba kafin jami’an su mayar da ita,” inji shaidan.
Daily Trust ta cewa bayan sun kai farmaki a gidansa, sun kuma je ofishin sa da ke Kaduna.
Wasu daga cikin Wadanda aka ceto wadanda harin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ya rutsa da su na ofishin Mamu kafin su sake haduwa da iyalansu.
Majiyoyin tsaro sun ce an kama Mamu ne bisa zarginsa da hannu wajen karbar kudin fansa da kuma kai makamancin haka ga ‘yan ta’adda domin musanya wadanda aka yi garkuwa da su.
Dimokuradiyya ta ruwaito yadda aka kama Mamu a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano a ranar Laraba da rana.
Mawallafin mazaunin Kaduna wanda aka fara kama shi a Masar an tsare shi tsawon sa’o’i 24 kafin a dawo da shi Najeriya.
