News
TIRƘASHI: Kansila ya naɗa muƙamai 32 a Kaduna
DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAHI
Abubakar Sadiq, Kansila mai wakiltar mazaɓar Saminaka a Ƙaramar Hukumar Lere a Jihar Kaduna, ya naɗa masu bashi shawara har guda 32.
Tuni dai takarda mai ɗauke da sunayen masu riƙe da mukaman da kuma ɓangarorin da za su jagoranta ta karaɗe kafofin sadarwa na zamani.
Ruwan Sama Da Kankara Ya Lalata Gonaki 300 A Katsina
Sai dai kuma da ya ke zanta wa da jaridar DAILY NIGERIAN, Kansilan ya ce ya naɗa waɗannan ɗumbin muƙamai ne domin ya rama alheri da alheri.
A cewar sa, duk waɗanda ya naɗa ɗin, su ne su ka tsaya tsayin-daka har sai da ya samu nasara, shi ya sa shima ya saka musu da irin soyayyar da su ke nuna masa.
Sadiq, wanda shine shugaban masu rinjaye na majalisar Ƙaramar Hukumar, ya ce biyan waɗannan ɗumbin ma’aikata nasa ba abu ba ne mai wahala domin tuni ya tanadi albashinsu da walwalarsu.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
