Connect with us

News

Tsaftar Muhalli: Mun Tanadi Kotunan Tafi Da Gidan Ka Ga Masu Kunnen Kashi – Kabiru Getso

Published

on

Getso

 

DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAH

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

Ma’aikatar muhalli ta jihar Kano ta ce shirye shirye sun kammala domin ganin an gudanar da tsaftar muhalli ta karshen wata da aka saba gudanar da ita a duka ranar asabar din karshen wata.

Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar Ismail Garba Gwammaja ne ya bayyana haka a ganawarsa da manema labarai, yana bukatar alumma da su bayar da hadin kai wajen zama a gida tare da tsaftace muhallansu, daga karfe 7 zuwa 10 na safe.

 

Ya kara da cewa sun tanadi jami’an tsaro a wannan karon kamar yadda aka saba, domin rangadi tare da tabbatar da kowa yabi dokar, da kuma hukunta wadanda suka bujire mata.

A nasa bangaren kwamishinan kula da muhalli na jihar Kano Dr Kabiru Ibrahim Getso ya ce tuni an tanadi kotunan tafi da gidanka, wadanda zasu hukunta duk wanda aka samu da laifin karyar dokar tsaftar muhallin ta gobe Asabar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending