News
An sako mahaifiyar ɗan majalisa bayan an biya kuɗin fansa
Daga Muhammad zahraddin
Masu garkuwa da mutane sun sako mahaifiyar shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Kano Isyaku Ali Ɗanja.
Ɗan majalisar ne ya tabbatarwa da Freedom Radio hakan da safiyar Talata.
Ya ce, an same ta a garin Gumel na jihar Jigawa kuma yanzu haka suna kan hanya domin ɗaukota.
Wasu rahotanni sun ce kafin sakinta dai da aka biya kuɗin fansa kimanin Naira Miliyan Arba’in.
A ranar 12 ga watan Janairun da muke ciki ne, ƴan bindiga suka kutsa kai kai har cikin gidanta a garin Ɗanja na ƙaramar hukumar Gezawa, inda suka yi awon gaba da ita
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
