Connect with us

Sports

Kungiyar Kwallon Kafa Ta Al-Nassr Ta Fara Zawarcin Kante

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr da ke kasar Saudiyya ta shiga zawarcin dan wasan Chelsea, Ngolo Kante.

 

Advertisement

Kwantaragin Kante zai kare da Chelsea a karshen kakar wasanni ta 2022, kuma kungiyar ba ta da ra’ayin sabunta kwantaragin dan wasan tsakiyar.

 

Advertisement

Hisbah Ta Rufe Wuraren Shan Giya Sama Da 100 A Zariya

Kante dai ya rasa gurbin zuwa Gasar Cin Kofin Duniya da aka kammala a Qatar sakamakon raunin da yake fama da shi.

 

Advertisement

Tsohon dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Leicester City, ba zai dawo murza leda ba sai Fabrairun 2023, amma hakan bai hana kungiyoyi fara zawarcinsa ba.

 

Advertisement

Duk da kungiyoyi da yawa da suka fara zawarcin Kante, amma ana tunanin Al-Nassr za ta iya daukar dan wasan duba da irin kudin da kungiyar ke shirin narkawa don daukarsa.

 

Advertisement

Jaridar Foot Mercato, ta rawaito cewar Al-Nassr ta shirya daukar dan wasan kafin kakar wasanni mai zuwa.

 

Advertisement

A baya-bayan nan, Al-Nassr ta zuba kudi masu yawa don daukar tsohon dan wasan Manchester United, Cristiano Ronaldo, bayan warware kwantaraginsa da kungiyar.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending