Connect with us

News

Sadakin Aure Kadai Za Mu Mayar — Lauyan Balaraba Ganduje

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Barista Ibrahim Aliyu Nassawara, lauyan da ke wakiltar ’yar Gwamnan Jihar Kano, Hajiya Asiya Balaraba Ganduje, ya shaida wa Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Filin Hoki a jihar cewa, sadakin Naira dubu 50 kadai za su mayar wa mijin Balaraba.

Advertisement

 

Wannan ya biyo bayan sharadin da lauyan mijin Balaraba Ganduje wato Alhaji Inuwa Uba, ya gindaya wa bangaren masu kara, inda ya ce bayan sadaki na Naira dubu 50 da suka biya suna kuma bukatar mai kara ta dawowa da mijnta wasu kayayyakinsa da ke hannunta.

Advertisement

 

 

Advertisement

A cewar Barista Umar I. Umar, akwai wasu motocinsa a wajenta da takardun karatunsa da kuma takardun kadarorinsa da suka hada da na gidaje da sauransu.

 

Advertisement

Daga cikin sharudan nasa ya nemi matar tasa ta sarayar da hakkinta na hadakar da suka yi wajen kafa wani kamfanin shinkafa.

 

Advertisement

 

“Idan tana bukatar ta fanshi kanta to ba maganar dawo masa da sadakinsa na naira dubu 50 ba ne kadai.

Advertisement

 

“Muna bukatar ta dawo masa da sauran kayayyakinsa da suka hada da takardun karatunsa da kuma takardun kadarorinsa.”

Advertisement

 

Sai dai a martanin da suka mayar lauyoyin mai kara karkarshin jagorancin Barista Ibrahim Aliyu Nassarawa, ya ce “Ba a yin khul’i a kan abin da yake a wajen aure.

Advertisement

 

“Wannan kaya da yake da’awa ba su shafi khulu’i ba.

Advertisement

 

 

Advertisement

“Shi khulu’i ana yinsa ne a kan abin da aka jingina aure

“Shi khulu’i ana yinsa ne a kan abin da aka jingina aure a kansa musamman sadaki amma ba wai a kan wani abu na daban ba.”

Advertisement

 

A cewar Barista Nassarawa, sadakin Naira dubu 50 za su mayar wa wanda ake kara.

Advertisement

 

“Kamata ya yi idan an kammala wannan shari’a sai ya nemi hakkinsa ta hanyar shigar da wata kara daban a kuma wata kotun ta daban.

Advertisement

 

“Amma mu a yanzu abin da muka sani shi ne Naira dubu 50 kuma shi kadai za mu biya.”

Advertisement

 

 

Advertisement

Bayan tafka zazzafar muhawara, dukkannin bangarorin biyu sun ki amincewa da juna.

 

Advertisement

Alkalin kotun Mai Shari a Khadi Abdullahi Halliru, ya ayyana 2 ga watan Fabrairu 2023 a matsayin ranar yanke hukunci.

 

Advertisement

Idan za a iya tunawa dai ‘yar gwamnan Kano, Asiya Balaraba Ganduje ce ta shigar da karar, inda ta nemi kotun ta datse igiyar aurenta na shekara 16 da mijinta, Alhaji Inuwa Uba.

 

Advertisement

Balaraba Ganduje ce dai ta shigar da karar mijin nata, tana rokon kotun ta raba aurensu ta hanyar Khulu’i, saboda ta gaji da zama da shi.

 

Advertisement

Sai dai mijin nata Inuwa Uba ta bakin lauyansa Barista Umar I Umar, ya ce sun yi iya kokarinsu na son ganin matar tasa kuma uwar ’ya’yansa guda hudu ta dawo dakinta amma abin ya ci tura.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending