Connect with us

News

Zargin Atiku: Keyamo Ya Maka EFCC Da ICPC A K

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Festus Keyamo, ya maka hukumomin yaki da rashawa na EFCC da ICPC a kotu, yana mai neman a kama tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar.

Advertisement

Babban lauyan, ya aike wa da EFCC da ICPC takarda kan lallai su kama dan takarar Shugaban Kasar na jam’iyyar PDP.

Mun Sha Kama Fitattun ’Yan Siyasa Masu Ta’ammali Da Miyagun Kwayoyi —Marw

Ya ce ya kamata a kama Atiku a gurfanar da shi a gaban kuliya bisa laifukan da ake zarginsa na yin sama da fadi da dukiyar al’umma.

Advertisement

Keyamo ya gabatar da wannan bukata ce bayan wani faifan sautin murya da Michael Achimugu, tsohon na hannun daman Atikun ya fitar.

A cikin faifan da aka saki makonnin da suka gabata, Achimugu ya yi zarge-zarge da dama a kan tsohon Mataimakin Shugaban Kasar.

Advertisement

Ya yi ikirarin cewa daga shekarar 1999 zuwa 2007 a lokacin da Atiku yake Mataimakin Shugaban Kasa, ya hada baki da tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo wajen halasta kudade.

A bisa wannan dalili ne Keyamo ya bukaci wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tilasta wa hukumomin yaki da rashawar su soma bincike tare da gurfanar da Atiku a gaban kuliya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending