News
’Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 11 A Syria
DAGA HAUWA KUNDILA
Sojoji 11 ne suka rasa rayukansu a hare-haren kungiyar ’yan ta’addan Tahri al-shamam kan yankin Arewa maso yammacin Syria ranar Laraba.
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Syria mai shalkwata a Birtaniya ta ce kungiyar ta harba roka da bama-bamai kan sansanin sojojin da ke Kafr Ruma , inda takwas da ke kusa da lardin Idlib suka rasu.
Rahotanni sun bayyana cewa daga baya ne ’yan ta’addan suka harbe karin sojoji uku a kusa da yankin Kafr Nahl da shi ma yake a lardin.
Yan ta’addan dai sun mamaye fiye da rabin yankin Idlib da sauran kewayen iyakar lardunan Aleppo, Hama da kuma Latakia.
Advertisements
