Connect with us

News

Sojoji Sun Cafke Ƴan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai A Kaduna Da Filato

Published

on

An yi wata musayar wuta tsakanin sojojin Najeriya da tawagar dan ta'adda Bello Turji

Sojojin Runduna ta 3 ƙarƙashin Operation SAFE HAVEN sun kama wani da ake zargin ɗan bindiga ne a Katsit, Zangon Kataf, da ke jihar Kaduna.

Wanda aka kama yana sanye da kayan soji, kuma ana zargin yana shirin kai hari da sace jama’a a yankin kafin a cafke shi.

Advertisement

Shirin Dangote Na Raba Mai Kyauta Zai Kassara Mu – Inji Dallalan Mai

An ƙwato bindigar AK-47, makami, harsashi 3, kwankon harsasai 7, katin ‘yan sa kai na bogi, waya da katin ATM guda biyu.

Sojojin sun miƙa wanda ake zargin hannun hukumomi domin ci gaba da bincike da daukar matakin shari’a a kansa.

Advertisement

A wani samame daban, sojoji sun kai farmaki maɓoyar masu safarar makamai a Kwanar Lauje, ƙaramar hukumar Bassa, jihar Filato.

Kodayake barayin sun tsere kafin isowar sojoji, amma an gano bindigu, harsashi 300 da kayan haɗa AK-47 da makaman harbo jirgin sama.

Advertisement

Har ila yau, sojoji sun ƙwato babur da ɓarayin suka bari a wajen; yayin da bincike ke ci gaba da gudana don kamo waɗanda suka tseren.

 

Advertisement

 

WIKKI TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending