Connect with us

News

Dole Ne a Karfafawa Likitoci Gwiwa Domin Su Zauna a Gidao Nijeriya – Obasanjo

Published

on

Ya kamata shugabannin Nijeriya da yawa su kasance a gidan yari Obasanjo
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce akwai buƙatar gwamnati da masu ruwa da tsaki su samar da kyakkyawan yanayin aiki da ƙarin ƙwarin gwiwa ga likitoci da nas da aka horas a cikin gida, domin kada su cigaba da barin ƙasar zuwa ƙasashen ƙetare.

Obasanjo ya bayyana haka ne a ranar Talata lokacin da yake buɗe asibitin Yariman Bakura da aka gyara a jihar Zamfara, ƙarƙashin gayyatar Gwamna Dauda Lawal.

Advertisement

Sojoji Sun Cafke Ƴan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai A Kaduna Da Filato

Tsohon shugaban ya nuna damuwarsa kan yadda matasa da dama ke barin Najeriya zuwa ƙasashen Turai, Amurka, Asiya da sauran yankuna domin samun rayuwa mafi inganci, lamarin da ake kira da “Japa”.

A cewarsa, wannan matsalar tana cigaba da haddasa giɓi a fannin lafiya, musamman ganin yadda ƙwararrun likitoci ke barin aiki a cikin gida.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending