News
Wurin bauta ya rufta da masu ibada a Indiya
Ƴan sanda na can suna kokarin kuɓutar da masu bauta da suka rufta a wani wurin bauta a yankin Madhya Pradesh da ke Indiya.
Mutane sun taru a wurin ne domin yin wani biki da aka saba yi mai suna Ram Navami.
An Kama Matashin Da Ake Zargi Da Yi Wa Jaririyar Wata 9 Fyade A Legas
Gidan bautan ya rufta ne bayan cikar da mutane suka yi a wurin, inda aka fitar da mutum takwas da suka faɗa cikin ruwa zuwa asibiti.
Kamfanin Dillancin Labaran ANI, ya ruwaito cewa tuni gwamnati ta soma gudanar da aikin ceto a wurin.
Babban ministan yankin Shivraj Singh Chouhan ya bayar da umarnin cewa a gaggauta aikin ceto domin fitar da mutanen da lamarin ya rutsa da su.
Ya ce yana magana da hukumomi a yankin na Indore don ganin aikinya tafi cikin sauri.
Mutane da lamarin ya faru a idonsu sun ce gwamman mutane ne suka rufta waɗanda galibi suka je don yin biki a wurin bautan.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
