News
Wurin bauta ya rufta da masu ibada a Indiya
Ƴan sanda na can suna kokarin kuɓutar da masu bauta da suka rufta a wani wurin bauta a yankin Madhya Pradesh da ke Indiya.
Mutane sun taru a wurin ne domin yin wani biki da aka saba yi mai suna Ram Navami.
An Kama Matashin Da Ake Zargi Da Yi Wa Jaririyar Wata 9 Fyade A Legas
Gidan bautan ya rufta ne bayan cikar da mutane suka yi a wurin, inda aka fitar da mutum takwas da suka faɗa cikin ruwa zuwa asibiti.
Kamfanin Dillancin Labaran ANI, ya ruwaito cewa tuni gwamnati ta soma gudanar da aikin ceto a wurin.
Babban ministan yankin Shivraj Singh Chouhan ya bayar da umarnin cewa a gaggauta aikin ceto domin fitar da mutanen da lamarin ya rutsa da su.
Ya ce yana magana da hukumomi a yankin na Indore don ganin aikinya tafi cikin sauri.
Mutane da lamarin ya faru a idonsu sun ce gwamman mutane ne suka rufta waɗanda galibi suka je don yin biki a wurin bautan.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
