Connect with us

News

Donald Trump Ya Musanta Dukkan Laifukan Da Ake Tuhumarsa Da Aikatawa

Published

on

Tsohon Shugaban Kasar Amurka, Donald Trump, kuma dan takarar jam’iyyar Republican a zaben 2024, ya musanta aikata laifuka 34 da ake tuhumarsa da aikatawa.

Trump ya ki amsa laifinsa ne lokacin da ya bayyana a kotun hukunta manyan laifuka ta Manhattan a ranar Talata a birnin New York, kamar yadda kafafen yada labarai suka rawaito.

Advertisement

Mutane 447 Ne Su Ka Kamu Da Cutar Amai-da-Gudawa a Jihohi 6 – NCDC

Tsohon shugaban ya shafe kusan awa biyu a kotun ana gudanar da bincike tare da gurfanar da shi a gaban kuliya.

Da yammacin Laraba ne ake sa ran zai koma Florida inda zai gabatar da jawabi a wajen taronsa na Mar-a-Lago, amma an tsare shi bayan halartar zaman kotun.

Advertisement

An gurfanar da shi a makon da ya gabata, Trump ya zama na farko a cikin tsoffin shugabannin Amurka da zai fuskanci tuhume-tuhume, kan shari’ar da ta shafi biyan kudi a 2016 ga tauraruwar fina-finan badala, Stormy Daniels.

A halin da ake ciki, sakataren yada labaran fadar White House a ranar Talata ta ki cewa komai kan tuhumar da ake yi wa Trump da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya.

Advertisement

Karine Jean-Pierre ta ki amsa duk wata tambaya kan tuhumar da ake yi wa Trump a yayin taron manema labarai.

A cewar Jean-Pierre, Joe Biden ya mayar da hankali ga jama’ar Amurka ne, ba abin da ya shafi maganar wani daban ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending