Connect with us

News

Yan bijilante za su kama saurayi da budurwa da ke zance a lokacin sallar Tahajjud

Published

on

Ƙungiyar Sintirin Bijilante dake Kano ɓangaren kwamandanta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta ce, ta ɗauki gaɓarar zuba jami’an ta a lungu da saƙo na Kano, domin tabbatar da tsaro a lokacin da za’a fara fita sallar dare ta Tuhajjud a yau Litinin, domin kawar da ɓatagari.

 

Jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar kuma Kwamandanta na shiyyar ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji ne, ya bayyana hakan ga manema labarai a daren Litinin.

Wasu  Yan Bindiga Sun Sace Basarake Da Wasu Mutum 13 A Abuja

Ya ce, ba za su saurarawa duk wasu ɓatagari dake fakewa da sallar dare suna aikata Laifuka ba.

 

 

Advertisement

 

 

A cewar sa, duk saurayi da budurwar da suka samesu a kan hanya ko lungu da sunan suna yin zance ko kuma yin abinda bai dace ba, zasu ɗauki matakin doka a kansu.

 

 

 

Advertisement

Ya kara da cewa kungiyar za ta zuba jami’anta a duk masallacin da ake sallar dare a Kano, domin tsare dukiyoyi da rayukan jama’a har ƙarshen sallar daren ta Tuhajjudin ba tare da gajiyawa ba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending