News
Gudun wuce sa’a ya haddasa mummunan haɗari a Kano
Daga muhammad muhammad zahraddin
Ana fargabar rasa ran wani direban mota sakamakon gudun wuce Sa’a da yake yi a safiyar ranar Asabar.
Haɗarin ya faru ne a titin Goron Dutse sakamakon taho mu gama da motoci biyu suka yi.
Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa guda daga cikin motar ita ce ta ke gudun wuce Sa’a wanda hakan ya sa ta je ta bige ɗaya motar da ke gabanta.
Sai dai tuni jami’an ƴan sanda da ke sintiri a yankin suka kai ɗauki tare da gaggawar kwashe waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti.
Wannan dai na zuwa ne yayin da ake duban tsaftar muhalli a yau Asabar, wanda hakan ya tilastawa tawagar tsaftar muhalli ta kai ɗaukin gaggawa wajen ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan muhalli Dakta Kabiru Ibrahim getso.
-
News6 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized2 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
