Connect with us

News

Wasu Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 40 A Kebbi Da Zamfara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

Akalla mutum 40 ne ’yan bindiga suka kashe, ciki har da jami’an tsaro, a jihohin Kebbi da Zamfara a ranar Lahadi.

 

Advertisement

Daga cikin mutanen da aka kashe har da ’yan sandan kwantar da tarzoma shida da fararen hula 36 a kauyen Dan Umaru da ke Karamar Hukumar Zuru a Jihar Kebbi.

Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa an gudanar da jana’izar mutum 27, wasu mutane da dama kuma sun samu raunuka a harin.

 

Sun bayyana cewa maharan sun kuma sace mutane da daruruwan dabbobi a kauyukan da ke makwabtaka da su.

 

A Jihar Zamfara kuma an kashe wasu mutum uku a wani kauye da ke Karamar Hukumar Shinkafi.

Advertisement

 

Sai dai har zuwa lokacin da muka kammala rubuta wanann labarin, hukumomin ’yan sanda ba su fiar ta bayani kan lamarin ba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending