News
Wasu Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 40 A Kebbi Da Zamfara
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Akalla mutum 40 ne ’yan bindiga suka kashe, ciki har da jami’an tsaro, a jihohin Kebbi da Zamfara a ranar Lahadi.
Daga cikin mutanen da aka kashe har da ’yan sandan kwantar da tarzoma shida da fararen hula 36 a kauyen Dan Umaru da ke Karamar Hukumar Zuru a Jihar Kebbi.
Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa an gudanar da jana’izar mutum 27, wasu mutane da dama kuma sun samu raunuka a harin.
Sun bayyana cewa maharan sun kuma sace mutane da daruruwan dabbobi a kauyukan da ke makwabtaka da su.
A Jihar Zamfara kuma an kashe wasu mutum uku a wani kauye da ke Karamar Hukumar Shinkafi.
Sai dai har zuwa lokacin da muka kammala rubuta wanann labarin, hukumomin ’yan sanda ba su fiar ta bayani kan lamarin ba.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
