Connect with us

News

Rundunar yan sanda ta ceto mutum 58 da aka yi garkuwa da su a Abuja

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Rundunar ‘yan sandan kasar nan  reshen Abuja  ta ce ta ceto mutum 58 da aka yi garkuwa da su.

Advertisement

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yan sandan Abuja SP Josephine Adeh ta fitar, ta bayyana cewa an ceto mutanen ne daga dajin Udulu da ke Karamar Hukumar Gegu ta Jihar Kogi, wanda ke da iyaka da Dajin Sardauna na Jihar Nasarawa.

Advertisement

 

Haka kuma ta ce akwai wasu da aka ceto daga wasu sansanonin ‘yan garkuwa da mutanen da aka gano a wasu wurare a Abuja.

Advertisement

NDLEA, ta ce ta kama tireloli biyu dauke da tabar wiwi a Legas

Sanarwar ta kara dace A lokacin da barayin suka ga jami’an tsaro karkashin jagorancin ‘yan sanda, sai suka soma harbinsu wanda hakan ya ja aka yi musayar wuta.

 

Advertisement

Daga  bindigar inda suka tsere da raunukan harsasai a jikinsu tare da barin wadanda suka kama,” in ji sanarwar.

 

Advertisement

Ta kara da cewa a lokacin aikin ceton, daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su mai suna Tama Jonathan ya rasu sakamakon raunukan da ya samu inda ya mutu a wurin nan take.

 

Advertisement

“An kai wa iyalinsa gawarsa domin a binne shi, sauran mutum 58 ana duba su a asibiti kuma za a hada su da iyalansu,” in ji sanarwar.

 

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa ta gudanar da wannan aikin ceton ne tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro da ‘yan bijilanti, duk a yunkurin kawo karshen garkuwa da mutane.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending