Connect with us

Business

Angola Ta Zarce Najeriya A Hako Danyen Man Fetur —OPEC

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Adadin danyen man da Najeriya ke hakowa ya ragu zuwa ganga dubu dari 9 da 99 a kowace rana a watan Afrilu.

Wannan lamarin dai ya sa yanzu Angola ta shiga gaban Najeriya saboda tana samar da ganga miliyan 1 da 63 a kowace rana.

Advertisement

Mutum biyu sun yi ba-hayar ƙulli 193 na hodar ibilis a hannun NDLEA

Wannan na kunshe ne a cikin rahoton wata wata na watan Afrilu da kungiyar kasashe masu arzikin danyen mai ta fitar a karshen makon da ya gabata.

Najeriya ta yi asarar gangunan danyen mai dubu 270 a watan Maris, kamar yadda alkalumman kungiyar OPEC din suka nuna.

Advertisement

OPEC ta ce gaba daya, mambobinta 13 na samar da gangunan mai miliyan 28 da dubu 60 a kowace rana a cikin watan da aka yi la’akari da shi wajen yin wannan rahoto.

Ta ce an samu karuwar danyen man da ake samarwa a Saudiyya, Angola da Iran, a yayin da aka samu akasin haka a Iraq da Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending