Connect with us

News

Sudan:Karin ‘yan Najeriya Sama Da 1,000 sun bar birnin Khartoum

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Wasu ‘yan Najeriya 1,350 a ranar Lahadin da ta gabata sun bar birnin Khartoum na Sudan da yaki ya daidaita zuwa Port Sudan inda za a dawo da su ta jirgin sama zuwa gida. Kamar yadda jaridar Nation ta ruwaito.

Advertisement

 

Port Sudan wani birni ne na Sudan mai tazarar kilomita 825 daga birnin Khartoum, inda har yanzu jirage za su iya sauka da tashi duk kuwa da yakin da ake yi tsakanin sojojin Sudan da dakarun Rapid Support Forces (RSF), karkashin jagorancin wasu janar-janar din soji guda biyu a rikicin neman mulkin kasar.

Advertisement

 

Rikicin Sudan: Sama da mutane dubu 20 suka tsallaka zuwa Chadi

 

Advertisement

Gwamnatin Tarayya ta yanke shawarar amfani da Port Sudan ne saboda matsalolin da rukunin farko na ‘yan Najeriya 637 suka fuskanta a kan iyakar Sudan da Masar.

 

Advertisement

Kashi na farko na mutanen da aka kwashe ana dawowa da su gida daga Alkahira babban birnin Masar.

 

Advertisement

Shugabar Hukumar Kula da Kasashen Waje ta Najeriya (NIDCOM) Misis Abike Dabiri-Erewa, a jiya ta tabbatar da jigilar rukuni na biyu na ‘yan Najeriya daga Khartoum.

 

Advertisement

 

Bayan an ba da izini, za a kwaso wadanda ke kan iyaka da Masar zuwa Najeriya daga filin jirgin saman Abu Simbel da jirgin saman Najeriya Air Force C-130.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending